Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP), Peter Obi, ya bi sahun Musulmi a babban masallacin Juma’a na Maraba-Nyanya a Abuja domin ayi buda baki da shi.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ɗan yi gyare gyare a naɗin tawagar waɗanda za su ja ragamar hukumar almajiri da yara marasa zuwa makaranta ta ƙasa.
Yayin da ake fama da matsalar 'yan bindiga a Arewa, Sheikh Ahmed Gumi ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta yi afuwa da kuma sulhu da maharan domin dakile rashin tsaro.
Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani, ya ƙaddamar da fara rabon kayayyakin agaji ga talakawa, gajiyayyau, marayu, mata da matasa karo na biyu a faɗin jihar ranar Litinin.
Wasu ɓarayin babura sun yi awon gaba da baburan jama'a yayin da ake tsaka da sallar tarawihi a kauyen Paso da ke ƙaramar hukumar Gwagwalada a Abuja.
Gwamna Mai Mala Buni ya amince da kashe Naira miliyan 100 na ciyar da marasa galihu abinci a kowane rana har karshen watan azumin Ramadan a jihar Yobe.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta wallafa jerin sunayen dakarun sojojin da wasu matada suka kashe a kauyen Okuama, karamar hukumar Ughelli a jihar Delta.
Hukumar EFCC ta sake bankado da maganar karkatar da kudin makamai da ake zargin tsohon shugaban PDP, halliru Bello a mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan.
A ranar Litinin ne Shugaba Tinubu, ya mika tutar jam’iyyar APC ga dan takarar gwamnan jihar Edo na jam’iyyar, Monday Okpebholo, da abokin takararsa, Dennis Idahosa.
Labarai
Samu kari