An dauki hoton wasu jami'an gwamnati su biyu suna zina

An dauki hoton wasu jami'an gwamnati su biyu suna zina

Hotunan wasu manyan jami'an gwamnatin Kenya su biyu sun watsu a kafar yanar gizo.

An dauki hoton wasu jami'an gwamnati su biyu suna zina

Duk da cewar ba'a san takamaimain wanda ya tona asirin ba, hotunan fasadin dai suna ta kara yaduwa, alokacin da suke mummunar yanayi, jami'an gwamnatin dai wa'anda dukkaninsu suna da aure kuma suna da yara, andai gansu ne suna cikin yanayi mara kyau.

Haka kuma, daya ma'ajine dayan kuma AP Ofisa ne wanda suke a Nakuru County wato Joseph Motari. Haka kuma, ma'aikatar Nukuru Public Service din ta tabbatar da cewar taga hotunan al'amarin kuma zata gudanar da bincike game da ma'aikatan guda biyu.

Ma'aikatar tasu tayi Allah wadai da zubar da mutuncin aikin su da sukayi, haka kuma ma'aikatar ta dakatar dasu daga zuwa aiki tun bayan da hotunan suka bazu a yanar gizo dakuma kafaffen yada labarai.

Sannan kuma, matar da akayi lalatar da ita taki cewa komai akan al'amarin, alokacin da kamfanin jaridar Star ta same ta game da aukuwar al'amarin.

Inda jarida tace gadai abunda matar tace mata kawai " ku kyaleni saboda baniso nayi magana da yawa tunda yanzu muna ganawar sirri da sauran uwana akan al'amarin".

Asali: Legit.ng

Online view pixel