Najeriya ta saki jerin sunayen nakassasu 23 na gasar Rio 2016

  Najeriya ta saki jerin sunayen nakassasu 23 na gasar Rio 2016

–Kwamitin wasannin nakassau ta Najeriya sun saki sunayen yan wasa 23 domin gasar

–Najeriya zatayi takara a wajen gudu, daga karfe, da ku tebur tanis

– Kwamitin wasannin nakassau ta Najeriya sun saki sunayen yan wasa 23 da zasu wakilci Najeriya a gasar Rio olymics da za’a yi a watan gobe.

   Najeriya ta saki jerin sunayen nakassasu 23 na gasar Rio 2016

Mai maganan kwamiin, Mr. Patrick Ibeh yace nakassasun zasuyi takarane kawai a wasanni guda 3, gudu, daga karfe,da kuma tebur tanis.

Mr. Ibeh ya bayyana cewa najeriya zata samu nasara a wasannin kuma kochnina 10 ne zasu raka su kasar Brazil. Wadanda zasu wakilci Najeriya a wasan gudu sune Hannah Babalola, Eucharia Iiazi,Laurettea Onye,Lovina Onyegbule da Flora Ugwunwa,yayinda Friday Aibange na kacal namiji a cikinsu.

   Najeriya ta saki jerin sunayen nakassasu 23 na gasar Rio 2016
Nigeria Paralympian

Wadan zasu wakilci najeriya a wasan daga karfe sune Nsini Ben, Lucy Ejike, Ndidi Nwosu, Bose Omolayo, Josephine Orji, Esther Onyema da Latifat Tijani a bangaren mata. A bangaren maza kuma sune Yakubu Adesokan, Roland Ezuruike, Abdulazeez Ibrahim, Nnamdi Innocent, Opeyemi Jegede, Paul Kehinde da Tolu-lope Taiwo

KU KARANTA : Rawar da Nigeria ta taka a gasar Olympics 2016

Zaku tuna cewa nakassasun najeriya sunci kyautar zinariya 6, azurfa 5 da kuma tagulla 2 a wasan Rio daya gabata a London 2012.

 

 

 

 

Asali: Legit.ng

Online view pixel