Dan wasan Najeriya Utaka ya samu tsaiko

Dan wasan Najeriya Utaka ya samu tsaiko

Tsohon dan wasan kungiyar Super Eagles dake wakiltar kasar Najeriya John Utaka ya samu tsaiko kasantuwar cinikin siyen sa da ya watse. A da dai dan wasan yana ta shirin komawa ne kungiyar kwallon kafa ta Ismaily daka kasar Egypt.

wakilin dan wasan dai Tekin Birinci shine ya bayyana haka a shafin sa na sada zumuntar zamani na Tuwita mai adreshin @tekinbirinci. Wakilin nasa yace: "John Utaka da kungiyar Ismaily basu cimma yarjejeniya ba. Yanzu haka yana a kasuwa ga duk wanda ke so."

Shi dai dan wasan mai shekaru 34 a yanzu ya taba buga wasa a kungiyar ta Ismaily a shekara ta 1999 inda ya taimaka mata wajen lashe kofin kasar na Egypt cup inda ya zura kwallaye 17 cikin wasanni 21 da ya buga.

Dan wasan Najeriya Utaka ya samu tsaiko
John Utaka set for Ismaily return

Daga bisani ne kuma sai ya tafi nahiyar turai ina ya buga kwallo a kungiyoyi da dama a kasar Ingila da ma Faransa ya kuma lashe kofuna da dama da shi din.

Asali: Legit.ng

Online view pixel