'Yan sanda sun kai mamaya gidan shugaban riko na jam'iyyar PDP, jihar Kano

'Yan sanda sun kai mamaya gidan shugaban riko na jam'iyyar PDP, jihar Kano

- 'Yan sanda sun kai mamaya gidan shugaban riko na jam'iyyar PDP, jihar Kano

- Sun je ne domin su hana shi gudanar ta taron da ya shirya

- Sun ce umurnin kotun jihar ne suka dabbaka

Jami'an rundunar 'yan sanda a jihar Kano mun samu cewa sun kai wata mamaya a gidan shugaban kwamitin riko na jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kano ranar Litinin din da ta gabata, 24 ga watan Satumba.

'Yan sanda sun kai mamaya gidan shugaban riko na jam'iyyar PDP, jihar Kano
'Yan sanda sun kai mamaya gidan shugaban riko na jam'iyyar PDP, jihar Kano
Asali: Facebook

KU KARANTA: Gwamnan Osun ya fadi ta cikin sa bayan sakamakon zabe ya fita

Su dai 'yan sandan kamar yadda muka samu, sun je gidan shugaban rikon ne dake a kan titin Sokoto dake garin na Kano inda suka tarwatsa 'ya'yan kwamitin da sauran magoya bayan jam'iyyar ta PDP a jihar Kano dake shirin gudanar da wani taro.

Legit.ng ta samu haka zalika cewa 'yan sandan dai sun yi hakan ne domin tabbatar da umurnin babbar kotun jihar da a baya ta yanke hukunci game da takaddamar shugabancin jam'iyyar a karshen watan jiya a Agusta.

Mai karatu dai zai tuna cewa a watan jiya ne kotun ta yanke hukuncin cewa kwamitin rikon da uwar jam'iyyar PDP ta nada a jihar Kano din haramtacce ne.

A wani labarin kuma, Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya shirya tsaf tomin yafewa wani tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bendel yanzu kuma jahohin Edo da Delta a Najeriya, Farfesa Ambrose Alli da aka zarga da hadame kudaden al'ummar jihar.

Mun samu cewa a lokacin mulkin shugaba Buhari na farko yana soja a shekarar 1983, wata kotu ta yankewa tsohon gwamnan wanda tuni ya mutu hukuncin dauri a gidan yari na shekaru 100 saboda samun sa da laifin karkatar da kudin yin wata hanya.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel