Tantiran tsagerun Neja Delta sun yi barazanar dagulawa Shugaba Buhari lissafi

Tantiran tsagerun Neja Delta sun yi barazanar dagulawa Shugaba Buhari lissafi

- Tsagerun Neja Delta sun yi barazana ga Shugaba Buhari

- Sun ce za su cigaba da kai hare-hare

- Sun yi kaca-kaca da jam'iyyar APC

Tantiran tsagerun nan na Neja Delta a karkashin wata gamayyar kungiyoyi da suka kira Coalition Niger Delta Agitators sun yi barazanar cigaba da kai sabbin hare-hare akan bututan mai dake a yankunan su idan dai har gwamnatin Buhari bata sake fasalin kasar nan ba.

Tantiran tsagerun Neja Delta sun yi barazanar dagulawa Shugaba Buhari lissafi
Tantiran tsagerun Neja Delta sun yi barazanar dagulawa Shugaba Buhari lissafi

KU KARANTA: Zamu kawo hari: Yan bindiga sun aika wasika zuwa garuruwa 4 a Arewa

Wannan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban gamayyar kungiyoyin Mista John Duku ya fitar dauke da sa hannun sa a ranar Asabar din da ta gabata a garin Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom.

Legit.ng ta samu cewa a cikin sanarwar, tsagerun sun yi Allah-wadai da irin salon mulkin jam'iyyar APC da sukace kwata-kwata yayi hannun riga da na demokradiyya tare da jan hankalin Shugaba Buhari da ya gaggauta biya masu bukatun su.

A wani labarin kuma, Yanzu haka dai harkokin tattalin arziki na cigaba da tabarbarewa yayin da baitul mali na Najeriya a babban bankin kasar watau Central Bank of Nigeria ya yi kasa da dalar Amurka miliyan 990 a cikin sati uku kacal da suka shude.

Wannan dai na kunshe ne a cikin rahoton da babban bankin ya fitar majiyar mu kuma ta Punch ta same shi a ranar Lahadin da ta gabata.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel