2019: Zan taka ko ina don ganin Saraki yayi nasara - Baraje

2019: Zan taka ko ina don ganin Saraki yayi nasara - Baraje

Tsohon mukaddashin shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Abubakar Kawu Baraje, yace a shirye yake ya taka rawar gani domin tabbatar da kudirin shugabancin shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki.

Baraje wadda ya kasance tsohon shugaban kungiyar sabuwar APC, yace a shirye yake da ya taka ko ina domin tabbatar da nasarar Saraki a zabe ai zuwa.

Ya bayyana hakan ne a wajen taron yaye dalibai na makarantar Islamiyyar sa wanda aka gudanar a ranar Alhamis, 16 ga watan Agusta a garin Ilorin, babban birnin jihar Kwara.

2019: Zan taka ko ina don ganin Saraki yayi nasara - Baraje
2019: Zan taka ko ina don ganin Saraki yayi nasara - Baraje

Ya kuma bayyana cewa Saraki ya dade da kaddamar da kudirinsa na takarar kujerar shugaban kasa, cewa kuma hakan ba laifi bane domin ya dade yana renon kudirin.

KU KARANTA KUMA: Kyawawan hotunan iyalan shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki, matarsa da yaransa

A baya Legit.ng ta rahoto cewa Shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki yace yana nazari akan yiwuwar tsayawarsa takarar shugaban kasa a zabe mai zuwa.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel