Wata sabuwa: Wani jigo a tafiyar Kwankwasiyya ya yi murabus daga mukamin sa

Wata sabuwa: Wani jigo a tafiyar Kwankwasiyya ya yi murabus daga mukamin sa

Yayin da muke ta kara matsewa shekarar zabe ta 2019, lamurra siysasa a kasar Najeriya na cigaba da kara zafafa inda 'yan siyasa da magoya bayan su ke ta kara daura damara domin cimma burin su.

Sai dai 'yan kwanaki kadan bayan ficewar fitaccen dan siyasar nan a yankin Arewa, tsohon gwamnan jihar Kano sannan kuma Sanata mai wakiltar mazabar Kano ta tsakiya dake zaman jagoran tafiyar Kwankwasiya daga APC zuwa PDP, siyasar kasar ta dauki wani sabon salo.

Wata sabuwa: Wani jigo a tafiyar Kwankwasiyya ya yi murabus daga mukamin sa
Wata sabuwa: Wani jigo a tafiyar Kwankwasiyya ya yi murabus daga mukamin sa

KU KARANTA: Jerin sunayen mutane 45 dake son hambarar da Buhari a 2019

Legit.ng ta samu cewa wani da ake kira Barista Bilyaminu Lukman Maihanchi dake zaman mai bayar da shawara akan harkar shari'a da dokoki na tafiyar kwankwasiyar a shiyyar Arewa maso gabashin Najeriya ya ajiye mukamin sa.

Barista Bilyaminu ya ce ya ajiye mukamin sa ne saboda shi har yanzu bai da gwanin da ya wuce shugaba Buhari a siyasa don haka ya dawo daga rakiyar Kwankwaso din.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel