An kori masu tsintar bola daga babban birnin tarayya Abuja

An kori masu tsintar bola daga babban birnin tarayya Abuja

Hukumar raya babban birnin tarayya, Abuja ta hanawa masu tsintar bola bi kan titinan birnin su na tsintar shara a kwandunan sharar kofar gidaje.

A wata sanarwa daga jami’in yada labaran Ministan Abuja, Abubakar Sani ya ce hakan ya biyo bayan korafe-korafen rahotannin sace-sace da ake zargin masu kwasar bolar na yiwa jama’a.

Sanarwar ta ce ana zargin su da aiwatar da kananan sace-sace, fashi da makami da sauran kananan laifukan da ba za a ci gaba da kauwar da kai a kan su ba.

Sakatariyar Hukumar Tsaftace birnin, Ladi Hassan, ta kara da cewa matasan da da aka fi sa Baban Bola, su na kuma yawan satar kayan gwamnati a wurare da dama, sannan kuma akwai su da kauda ajiyar da ba su ne suka yi ba.

An kori masu tsintar bola daga babban birnin tarayya Abuja
An kori masu tsintar bola daga babban birnin tarayya Abuja

Daga nan ta shaida cewa an amince su yi harkokin Baban Bola a garuruwan Gousa, Karshi, Bwari, Gwagwalada, Kwali, Abaji da Kuje.

KU KARANTA KUMA: Dalilin da ya sa na halarci taron sanatocin APC da shugaba Buhari – Shehu Sani

A karshe ta yi kira ga jami’an tsaro su kama tare da gurfanar da duk wanda suka kama ya na tsintar bola a cikin birnin Abuja.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel