2019: INEC ta nada sabbin kwamishinonin zabe a jihohin arewa 2, duba hotuna

2019: INEC ta nada sabbin kwamishinonin zabe a jihohin arewa 2, duba hotuna

A yau, Laraba, ne shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmoud Yakubu, ya nada tare da rantsar da sabbin kwamishinonin zabe 2 da ya nada.

Sabbin kwamishinonin 2 da aka nada zasu yi aiki ne a jihohin arewa 2 da suka hada da Naija da Zamfara.

Sabbin kwamishinonin zaben sune; Ahmad Bello Mahmud (Jihar Zamfara) da Garba Attahiru Madami (jihar Neja).

2019: INEC ta nada sabbin kwamishinonin zabe a jihohin arewa 2, duba hotuna
Garba Attahiru Madami ke karbar rantsuwa

2019: INEC ta nada sabbin kwamishinonin zabe a jihohin arewa 2, duba hotuna
Ahmed Bello Mahmoud ke karbar gaisuwa

An rantsar da sabbin kwamishinonin ne a ofishin hukummar zabe na kasa dake birnin tarayya, Abuja.

DUBA WANNAN: Jerin sunayen 'yan majalisar dokoki 6 na jihar Kano da zasu bi Kwankwaso PDP

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmoud, ya taya su murna zabensu da kuma tabbatar da su a matsayin sabbin kwamishinoni tare da yin kira garesu su kasance masu riko da rantsuwar suka yin a yin aiki da gaskiya da rikon amana.

2019: INEC ta nada sabbin kwamishinonin zabe a jihohin arewa 2, duba hotuna
sabbin kwamishinonin zaben jihohin Neja da Zamfara

2019: INEC ta nada sabbin kwamishinonin zabe a jihohin arewa 2, duba hotuna
INEC ta nada sabbin kwamishinonin zabe

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel