Mahakurci mawadaci: Buhari ya nada Naja’atu Muhammad wani muhimmin mukami

Mahakurci mawadaci: Buhari ya nada Naja’atu Muhammad wani muhimmin mukami

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada tsohuwar yar gwagwarmaya, Hajiya Naja’atu Muhammad mukamin mamba a hukumar gudanawa ta hukumar Yansandan Najeriya, kamar yadda Legit.ng ta ruwaito.

Shugaba Buhari ya yi wannan nadi ne fadar shugaban kasa dake babban birnin tarayya Abuja a ranar Laraba, 25 ga watan Yuli, inda ya kaddamar da hukumar gudanarwar tare da yayanta.

KU KARANTA: Karyar banza: Amurka ta soki kasashen Musulmai kan rashin tallafa ma Falasdinu

Mahakurci mawadaci: Buhari ya nada Naja’atu Muhammad wani muhimmin mukami
Hajiya Naja

Tsohon babban sufetan Yansandan Najeriya, Alhaji Musiliu Smith ne aka nada shugaban wannan hukumar, sai kuma Najatu Mohammed a matsayin wakiliyar Arewa maso yamma, Braimoh Austin kudu maso kudu, da Rommy Mom Arewa ta tsakiya.

Sauran mambobin wannan hukuma sun hada da Nkemka Jombo-Ofo wakilin Kudu maso gabas, Clara Ogunbiyi wakiliyar kudu maso yamma da AIG Lawal Bawa a matsayin wakilin Arewa maso gabas.

Mahakurci mawadaci: Buhari ya nada Naja’atu Muhammad wani muhimmin mukami
Nadin Naja

Ita dai Naja’atu ta kasance tsohuwar shahararriyar mai goyon bayan shugaban kasa Buhari tun daga shekarar 2003 zuwa 2007 da ya tsaya takara, amma a shekarar 2011 bata yi Buhari ba, sai ta kafa tanti da Nuhu Ribadu dan takarar jam’iyyar ACN, har sai a 2015, inda suka dinke barakar dake tsakaninsu.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel