Oshiomhole zai tabbatar da nasarar Buhari a 2019: Fayemi

Oshiomhole zai tabbatar da nasarar Buhari a 2019: Fayemi

Gwamnan jihar Ekiti mai jiran gado, Dr Kayode Fayemi yace da nasarar da yayi a ranar 14 ga watan Yuli, 2018, shugaban jam’iyyar APC mai mulki, Kwamrad Adams Oshiomhole zai sake nasara a zaben jihar Osun mai zuwa da kuma zaben shugaban kasa da za’a yi a ranar 16 ga watan Fabrairun 2019.

Fayemi wadda yayi Magana a jiya a Aubuja a sakatariyar APC na kasa bayan ganawa da Oshiomhole, ya bayyana sauya shekar wasu yan majalisun dokokin kasar a matsayin “damokradiyya a aikace”.

A cewarsa sauya shekarsu bai tada hankalin jam’iyyarsu ba ko kadan, domin sun yarda da kansu da kuma shugabancin jagoransu.

Oshiomhole zai tabbatar da nasarar Buhari a 2019: Fayemi
Oshiomhole zai tabbatar da nasarar Buhari a 2019: Fayemi

Ya jadadda cewa siyasa ta gaji haka yayinda ake kulle wasu kofofi haka ake bude wasu.

KU KARANTA KUMA: Yayinda yan majalisa da yawa suka sauya sheka a APC, gwamnoni sun yunkura domin ceto jam’iyyar

Tsohon ministan ma’adinai yace ziyarar da ya kai hedkwatar jam’iyyar ba komai bace face ziyarar ban girma. Cewa wannan ne karo na farko day a ziyarci sakatariyar tunda Oshiomhole ya karbi shugabancin jam’iyyar.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel