"Budurwa ta ta fesbuk ta goga mun kanjamau" - Wani saurayi ya bada labari

"Budurwa ta ta fesbuk ta goga mun kanjamau" - Wani saurayi ya bada labari

Wani ma'abocin anfani da kafar sadarwar zamani ta Fezbuk mai suna Ola O'Neil da ke da adreshin (@_gal2) a dandalin Tuwita ya fito fili ya fadawa duniya yadda wata budurwar da yayi a kafar sadarwar zamani ta Fezbuk ta goga masa cutar kanjamau.

Mutumin dai wanda ya zayyana cewa haduwar sa da budurwar ke da wuya a kafar sadarwar zamanin cikin kasa da sati daya har sun shirya haduwa a otel inda kuma suka kwanta da juna.

"Budurwa ta ta fesbuk ta goga mun kanjamau" - Wani saurayi ya bada labari
"Budurwa ta ta fesbuk ta goga mun kanjamau" - Wani saurayi ya bada labari

KU KARANTA: Za'ayi anfani da jiragen yaki wajen rabon kyan zabe a 2019

Legit.ng ta samu cewa daga nan ne kuma sai ya shawarci dukkan samari da 'yan mata da su yi taka tsan-tsan game da rayuwa kuma su bi a hankali kar su jefa kansu cikin nadama da na sani irin wadda ya shiga.

A wani labarin kuma, Gamammiyar kungiyar kiristocin Najeriya 'yan asalin Arewa da ke da mambobin ta a dukkan jahohin yankin 19 sun yi tofin Allah-tsine ga hadimar shugaban kasa Muhammadu Buhari mai suna Lauretta Onochie.

Kungiyar dai ta ce abun takaici ne yadda hadimar tayi anfani da kalamai munana ga 'ya'yan kungiyar inda ta siffanta su da 'tsutsotsi' a shafin ta na sadarwar zamani ta Tuwita.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel