Shehunnan malaman addinin kirista sun bukaci Shugaba Buhari yayi murabus

Shehunnan malaman addinin kirista sun bukaci Shugaba Buhari yayi murabus

Shehunnan malaman addinin kirista a Najeriya jiya sun bukaci shugaban kasar Najeriya da yayi murabus ko kuma ya tabbatar da samar da kyakkyawan tsaron da zai ba jama'ar kasar nan kariya daga kashe-kashe.

Babban Rabaran din Dakta Martin Uzoukwu da yayi magana a madadin sauran 'yan uwan sa yayin wani gangamin nuna rashin jin dadi game da kisan 'yan uwan su manyan malamai a jihar Benue ya bayyana cewa ba za su lamunci cigaba da kisan na su ba.

Shehunnan malaman addinin kirista sun bukaci Shugaba Buhari yayi murabus
Shehunnan malaman addinin kirista sun bukaci Shugaba Buhari yayi murabus

KU KARANTA: Kiristoci sun yi wa Buhari zanga-zanga a Abuja

Legit.ng dai ta samu cewa jiya ne dubun dubatar kiristocin kasar nan suka fita saman tituna a manyan biranen Najeriya suna masu zanga-zangar kisan su da suka ce ana yi a kasar nan.

A wani labarin kuma, Shugaba Muhammadu Buhari a jiya ya bayyana cewa kawo yanzu kudaden ajiya na kasashen waje ko baitulmalin Najeriya ya kai akalla $47 biliyan tun 9 gawan Afrilu sabanin $29.6 biliyan din da suka samu kasar a watan Mayu na shekarar 2015.

Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron karrama wasu zakakuran Najeriya na rukunin National Productivity Order of Merit (NPOM) a turance da ya gudana a garin Abuja.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da Kuma

Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel