'Yan ta'addan Houthi sun sake kai wa Saudiyya hari da makami mai linzami

'Yan ta'addan Houthi sun sake kai wa Saudiyya hari da makami mai linzami

'Yan ta'addar Houthi 'Yan Shi'a da ke Kasar Yaman sun sake kai hari ga Saudiyya da makamai masu linzami 3 ammasai dai an yi amfani da garkuwa wajen bata makaman tun kafin fadowarsu.

Tashar talabijin ta Al-Akhbariyya ta bayyana cewa, an kai harin da makamai 2 zuwa garin Riyadh inda dayan kuma a ka kai garin Jazan inda aka bata su dukka tun kafin su fado.

'Yan ta'addan Houthi sun sake kai wa Saudiyya hari da makami mai linzami
'Yan ta'addan Houthi sun sake kai wa Saudiyya hari da makami mai linzami

Tashar Al-Misira ta mayakan Houthi kuma ta ce, sun kai harin ne da makamai samfurin Volcan-2.

KU KARANTA KUMA: Farashin Man Fetur ya tumfaya a Kasuwannin Duniya, Amurka ta janye alakar ta da Kasar Iran

An bayyana cewa, an kai harin garin Jazan da makami samfurin bedir.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel