An ba hamata iska tsakanin sojojin Najeriya da jami'an tsaron farar hula na NSCDC

An ba hamata iska tsakanin sojojin Najeriya da jami'an tsaron farar hula na NSCDC

Barikin sojoji ta 16 dake zaman ta a garin Yenagoa babban birnin jihar Bayelsa dake a shiyyar kudu-maso-kudancin kasar nan a jiya mun samu labarin cewa sun ba hamata iska tsakanin sun da jami'an tsaron farar hula.

Kamar dai yadda muka samu duka rigimar ta auku ne sakamakon wata babbar mota shakare da manfetur da jami'an tsaron farar hula na NSCDC suka kama suna kuma kokarin kai ta hedikwatar su kafin daga bisanin sojojin su bukaci kwace motar daga hannun su.

An ba hamata iska tsakanin sojojin Najeriya da jami'an tsaron farar hula na NSCDC
An ba hamata iska tsakanin sojojin Najeriya da jami'an tsaron farar hula na NSCDC

KU KARANTA: Fitaccen dan siyasa ya sha da kyal bayan ya goyi bayan tazarcen Buhari

Legit.ng ta samu cewa tuni dai dangantaka tayi tsami a tsakanin jami'an tsaron biyo bayan martanin zafafan kalaman da sukayi ta maidawa junan su kan lamarin.

A wani labarin kuma, Kamar dai yadda watakila kuka samu labari cewa a jiya shugaba Muhammadu Buhari ya saka labule da shugabannin majalisar tarayyar Najeriya da suka hada da Honarabul Yakubu Dogara da kuma Sanata Bukola Saraki a fadar sa dake a unguwar Aso Rock, babban birnin tarayya Abuja.

Sai dai majiyar mu ta labarta mana cewa jim kadan bayan kammala ganawar, shugabannin majalisar sun bayyanawa yan jarida muhimman batutuwan da suka tattauna da shugaban kasar.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel