Boko Haram: Sojojin Najeriya sun samu galaba kan ‘Yan ta’adda a Yobe

Boko Haram: Sojojin Najeriya sun samu galaba kan ‘Yan ta’adda a Yobe

Labari ya kai gare mu cewa Rundunar Sojojin Najeriya da ke yaki da ‘Yan ta’adda a kasar sun damke wasu mutane har 4 da ake zargi ‘Yan Boko Haram ne a wasu Garuruwa a cikin Jihar Yobe.

Wadanda ake zargi da cewa ‘Yan ta’addda ne sun fada hannun Sojojin Operation Lafiya Dole ne a Ranar Juma’ar nan 27 ga Watan Afrilu kamar yadda Darektan yada labarai na gidan Sojin kasar Birgediya Janar Texas Chukwu ya bayyana.

Boko Haram: Sojojin Najeriya sun samu galaba kan ‘Yan ta’adda a Yobe
Daya daga cikin wadanda aka kama a Garin Fune

Janar Texas Chukwu ya bayyana sunayen wadanda aka kama da kuma kayan da aka samu a hannun su. Bataliya ta 223 na Operation LAFIYA DOLE ce dai tayi wannan namijin kokari a Garin Damagun da ke cikin Karamar Hukumar Fune.

KU KARANTA: Wani Matashi yayi barna a Kudancin Najeriya

Boko Haram: Sojojin Najeriya sun samu galaba kan ‘Yan ta’adda a Yobe
Wani wanda Sojojin Najeriya su ka damke a Yobe

Ga sunayen wadanda aka kama da adadin shekarun su:

1. Chari Masaa (shekaru 40)

2. Gonbuzu Abar (shekaru 30)

3. Modu Moduchollo (shekaru 20)

4. Titta Masawa (shekaru 20)

Bayan nan kuma an kama wani mai daure-masu gindi mai suna Gambo Idrissa mai shekara 30 a Duniya.

Daga cikin abubuwan da aka samu daga hannun su akwai

1. Wayoyin zamani kirar Techno 4

2. Makudan kudi har N150, 000

Dama kuma kafin nan Sojojin da ke Garin Fatiskum sun kama wani ‘Dan ta’addan mai suna Salisu Musa ‘dan shekara 30 a Kauyen Sabon Gari Duddaye da ke cikin Nangere.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel