Aikata baɗala a gidajen kallon kwallo: Sarkin Kano ya baiwa Daurawa muhimmin aiki

Aikata baɗala a gidajen kallon kwallo: Sarkin Kano ya baiwa Daurawa muhimmin aiki

Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sunusi II ya umarci shugaban hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Daurawa da ya binciko hakikanin gaskiyar zarge zargen da ake yadawa a gari na cewar matasa na tafka ta’asa iri iri a gidajen kallon kwallo a jihar Kano.

Jaridar Puncj ta ruwaito Sarkin Kano ya samu rahotannin dake bayyana cewa matasan unguwannin Badawa, Kawo, Sauna da Haye, suna tafka ayyukan masha’a daban daban da sunan zuwa kallon kwallo.

KU KARANTA: Wani jami’in Dansanda ya rasa ransa a yayin wani hari da yan bindiga suka kai Ofishin Yansanda

Mazauna unguwannin ne suka kai korafi ga Sarkin, inda suka ce wani gidan kallon kwallo da wani attajiri, Auwalu Sankara ya bude ya zama tashar yan iska, inda matasa bata gari ke sheke ayarsu son rai ba tare da kwaba ba.

Aikata baɗala a gidajen kallon kwallo: Sarkin Kano ya baiwa Daurawa muhimmin aiki
Ssarki

Shugaban mazauna unguwannin, Mohammed Al-Hassan ya bayyana cewa gurbatattun matasa sun mayar da gidan kallon kwallon wata mafaka da duke siya da siyar da kwayoyi da sauran kayan shaye shaye.

Da yake tattaunawa da tawagar mazauna unguwannin, Sarki Muhammadu Sunusi II yay aba da kokarin da suke yi na sanya idanu tare da kuma tabbatar da zaman lafiya a unguwanninsu, sa’annan ya basu tabbacin hukumar Hisbah zata kamo duk masu hannu cikin lamarin.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel