An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka

An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka

- An tabbatar da mutuwar wasu matasa biyu a unguwanni daban-daban dake cikin garin Bauchi

- Matasan sun rasa rayukan su ne a unguwannin Jahun da titin Wanka a garin Bauchi sakamakon rikici a kan lika fostar zabe

- Mazauna titin Wanka sun ce an kashe wani matashi a kofar gidansu kuma tuni har an binne shi bisa tsarin addinin Islama

An tabbatar da mutuwar wasu matasa biyu a unguwanni daban-daban dake cikin garin Bauchi.

Matasan sun rasa rayukan su ne a unguwannin Jahun da titin Wanka a garin Bauchi sakamakon rikici a kan lika fostar zabe.

Mazauna titin Wanka sun ce an kashe wani matashi a kofar gidansu kuma tuni har an binne shi bisa tsarin addinin Islama.

An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka
An zo wurin: Matasa sun tafka rikicin siyasa a jihar Bauchi, an rasa rayuka

Wani shaidar gani da ido, Mohammed Adam, ya shaidawa jaridar Daily Post cewar an kashe matasan ne a kan rikicin lika fostar zabe ko kuma cire ta.

Kakakin hukumar 'yan sanda a jihar Bauchi, DSP Datti Kamal, ya tabbatar da afkuwar lamarin ga Daily Post.

DUBA WANNAN: Jirgin yakin hukumar soji MI-35M ya yi ruwan nakiyoyi a kan motocin 'yan Boko Haram

A cewar sa, "mun samu rahoton kisan wani matashi, Abdulhaxiz Yunusa, da wasu matasa da ba a san ko su waye ba suka aikata a kofar gidansa."

Ya kara da cewar hukumar 'yan sanda na gudanar da bincike domin gano wadanda keda hannu cikin kisan.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel