Dalilin da yasa muka caccaki Buhari a babban masallacin tarayya – Yan Shi’a

Dalilin da yasa muka caccaki Buhari a babban masallacin tarayya – Yan Shi’a

Yan kungiyar IMN da aka fi sani da yan Shi’a sun tabbatar da cewa lallai mambobinsu ne suka caccaki shugaba Muhammadu Buhari ranan Juma’an da ya gabata a babban masallacin tarayya, Abuja.

Kafafen yada labarai sun bada rahoton cewa wasu mabiya Shi’a sun yi zanga-zanga a masallacin Juma’a inda shugaba Buhari ya zo Sallah amma fadar shugaban kasa ta musanta hakan.

Dalilin da yasa muka zazzagi Buhari a babban masallacin tarayya – Yan Shi’a
Dalilin da yasa muka zazzagi Buhari a babban masallacin tarayya – Yan Shi’a

Kungiyar ta ce mambobinta sun dau wannan mataki ne saboda shugaba Buhari ya ki sakin shugabansu, Ibrahim El-Zakzaky bayan shekaru 2 yanzu.

KU KARANTA: Za’a gurfanar da Dino Melaye tare da yan bindiga 4 ranan 10 ga Mayu

A wani hira da mamban kungiyar Abdullahi Muhammad Musa ya gabatar, ya ce suna zanga-zangan lumana ne domin nuna zaluncin gwamnatin tarayya da cutan hukumar sojin Najeriya.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

Asali: Legit.ng

Online view pixel