Sabbin masana'antun wutar lantarki 4 za su fara aiki gadan-gadan a Najeriya

Sabbin masana'antun wutar lantarki 4 za su fara aiki gadan-gadan a Najeriya

Kimanin kusan wutar lantarkin da ta kai yawan 1,262 na ma'aunin Mega wat ne zai karu a Najeriya nan da alkalla watanni hudu indai har sabbin masana'antun wutar lantarkin kasar suka soma aiki gadan-gadan.

Mun samu daga majiyar mu dai cewa kawo yanzu aski yazo gaban goshi wajen ganin cewa masana'antun wutar lantarkin wadanda dukkanin su suna a yankin Neja Delta ne za a fara aikin gwajin su ne a cikin satukan nan masu zuwa.

Sabbin masana'antun wutar lantarki 4 za su fara aiki gadan-gadan a Najeriya
Sabbin masana'antun wutar lantarki 4 za su fara aiki gadan-gadan a Najeriya

KU KARANTA: An fara shirin yiwa Sanatocin jihar Kaduna kiranye

Legit.ng dai ta samu cewa sabbin masana'antun na wutar lantarkin sun hada da ta garin Gbarain sai ta garin Aloji da kuma ta garin Omoku sannan daga karshe ta garin Afam.

A wani labarin kuma, Wasu matasa a jihar Kaduna da suka ce suna rajin kare talaka da kuma matukar damuwa da jihar a karkashin inuwar kungiyar Kaduna Concerned Citizens ta ayyana cewa 'ya'yan ta tuni suka fara shire-shiren yi wa 'yan majalisar dattawan jihar kiranye.

Kamar dai yadda suka bayyana cewa sun fara hakan ne sakamakon korafe-korafe da kuma goyon bayan da suka samu daga al'ummar jihar musamman ma dai ganin cewa Sanatocin a cewar su ba su kaunar jihar ko kadan musamman ma ganin yadda suka hakan jihar cin bashin $ miliyan 350 daga bankin duniya.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel