Hijab : Wani mallamin addini yayi kira da gwamnatin tarayya ta tabbatar da kare hakkokin musulmi a Najeriya

Hijab : Wani mallamin addini yayi kira da gwamnatin tarayya ta tabbatar da kare hakkokin musulmi a Najeriya

- Limamnin masalcin Garki yayi kira da gwamnatin tarayya ta tabbatar da kare hakkokin musulmi a Najeriya

- Sheikh Yahya Al-Yolawi ya bayyana damuwar sa akan yadda ake cin zarafin mata masu sanya hijabi a Najeriya

Wani Bbbbabn mallamin addinin musulunci mazaunin garin Abuja, Sheikh Yahya Al-Yolawi, yayi kira da gwamnatin tarayya ta tabbatar da kare hakokin musulmai a kasar

Shehin Mallamin, yayi wannan kira a wata hira da yayi da majiya jaridar News Agency of Nigeria (NAN) a ranar Laraba.

Sheikh Yahya Al-Yolawi shine limamin babban masallacin Area 10, dake Garki Abuja.

Hijab : Wani mallamin addini yayi kira da gwamnatin tarayya ta tabbatar da kare hakkokin musulmi a Najeriya
Hijab : Wani mallamin addini yayi kira da gwamnatin tarayya ta tabbatar da kare hakkokin musulmi a Najeriya

Yace, ya zama dole gwamnati tarayya ta hana cin zarafin matan dake sanya hijabi a fadin kasar, saboda sanya hijab wajibi ne ga mata a adinin musulunci.

KU KARANTA : Fusatattun matasa sun kona barawon waya a jihar Nasarawa

Mallamin ya bayyana damuwar sa akan yadda cin zarafi mata masu sanya hijabi a kasar ya zama ruwan dare

“Ya zama dole shugabanin musulmai su tashi tsaye su kare hakokin musulmai a cikin kasar nan," inji Sheikh Yahya Al-Yolawi.

Dannan wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel