HND/Digiri: Mun cire rashin daidaito a tsarin aikin gwamnati - Buhari

HND/Digiri: Mun cire rashin daidaito a tsarin aikin gwamnati - Buhari

- Gwamnatin Tarayya: Mun cire babanci tsakanin HND, da BSc, daga aikin tarayya

- Gwamnatin tarayya ta cire babanci tsakanin masu takardaun HND, da kuma BSc, daga ka’iadar aikin kwamnatin tarayya

- Gwamnatin ta karfafa albashin farkon daukar aiki ta mayar dashi daga mataki na 7 zuwa na 8 ga masu HND

- Sakataren Harkokin Kasuwanci, Harkokin Gudanar da Tsarin Ayyuka (SPSO), Ofishin Jakadancin Tarayya, Mr Ndubuisi Osuji, ya sanar da wannan

HND/Digiri: Mun cire rashin daidaito a tsarin aikin gwamnati - Buhari
HND/Digiri: Mun cire rashin daidaito a tsarin aikin gwamnati - Buhari

Gwamnatin tarayya ta cire babanci tsakanin masu takardaun HND, da kuma BSc, daga ka’iadar aikin kwamnatin tarayya. A ka’idance, Gwamnatin ta karfafa albashin farkon daukar aiki ta mayar dashi daga mataki na 7 zuwa na 8 ga masu HND.

Sakataren Harkokin Kasuwanci, Harkokin Gudanar da Tsarin Ayyuka (SPSO), Ofishin Jakadancin Tarayya, Mr Ndubuisi Osuji, ya sanar da wannan a lokacin taron majalisar tarayya na 40, a Owerri, jihar Imo.

Yace, wannana yayi daidai da shawarar da aka yanke a taron majalisar tarayya na 39 akan bunkasa rayuwar ma’aikata. Wannan ya biyo cikin wani bayani daya fito a ranar Alhamis, a Birnin Tarayya, daga Mataimakin Daraktan labarai, Ofishin Jakadancin Tarayya, Mr Timothy Akpoli, a matsayin mai wakilcin Daraktan Sadarwa.

DUBA WANNAN: Mace da ta fi kowa kudi a Afirka

An ruwaito cewa Mr Osuji, yace, an yanke shawarar ne a lokacin taron NCE na 39 ta hanyar rarraba takardun zuwa ga masu ruwa da tsaki.

Wannan, ya lura, zai ciima buri mai muhimmanci na samar da takardar shaida guda daya ga duka matakai na masu aiki kanana dama kwararru, da kuma rage yawan hukunce-hukuncen da majalisa ke yankewa.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel