'Yan bindiga sun kai hari kan wani jirgin kasa a garin Kaduna

'Yan bindiga sun kai hari kan wani jirgin kasa a garin Kaduna

Mun samu rahoton cewa, a ranar Talatar da ta gabata ne wasu 'yan ta'adda suka kai kari kan wani jirgin kasa dauke da daruruwan fasinjoji a kauyen Rijana yayin da yake kan hanyar sa ta zuwa Rigasa a jihar Kaduna.

Daya daga cikin ma'aikatan jirgin Olusegun Giwa ya bayyana cewa, harin ya afku ne da misalin karfe 7.00 na yammacin ranar Talatar a kilomita 70 zuwa cikin birnin Kaduna.

'Yan bindiga sun kai hari kan wani jirgin kasa a garin Kaduna
'Yan bindiga sun kai hari kan wani jirgin kasa a garin Kaduna

Rahotanni sun bayyana cewa, manyan 'yan siyasa da jiga-jigan gwamnati sun fara bibiyar jiragen kasa sakamakon 'yan ta'addan masu garkuwa da mutane da suke addabar manyan hanyoyin kasar nan.

KARANTA KUMA: Kiwon Lafiya: Amfanin 'Kimchi' 8 ga lafiyar dan Adam

Maharan dai sun budewa jirgin wuta da harsashai na bindiga, inda aka yi sa'a an yi masa garkuwa harsashi yayi kera shi da ya sanya ba bu wani rauni ko asarar rayuka da dukiya da ta afku.

Legit.ng ta kuma ruwaito wasu sirrika 7 na ruwan Zam-Zam da ya kamata kowane musulmi ya ribaci ilimin sa.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Domin shawara ko buƙatar bamu labari, tuntuɓe mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://facebook.com/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel