Rikicin kasuwan magani: Gwamnatin jihar Kaduna ta gurfanar da mutane 63 a kotu

Rikicin kasuwan magani: Gwamnatin jihar Kaduna ta gurfanar da mutane 63 a kotu

- Gwamnatin jihar Kaduna ta gurfanar da mutane 63 a kotu akan rikicin kasuwar magani

- Rikicin kasuwan magani yayi sanadiyar mutuwar mutane 12 da asarar dukiyoyi

Idan ba a manta ba a makon da ya gabata ne gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya umurci jami’an tsaron jihar da su taso masa keyar wadanda suka tada rikicin Kasuwar Magani dake Kajuru, jihar Kaduna.

A makon da ya gabata ne gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir Ahmed El-Rufai, ya umarci jami’an tsaron jihar, da su taso masa keyar mutanen da suka haddasa rikicin da aka yi a Kasuwar Magani wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane 12 da asarar dukiyoyi masu dimbin yawa.

Rikicin kasuwan magani : Gwamnatin jihar Kaduna ta gurfanar da mutane 63 a kotu
Rikicin kasuwan magani : Gwamnatin jihar Kaduna ta gurfanar da mutane 63 a kotu

Gwamnatin jihar Kaduna ta maka mutane 63 a kotu wadanda akae zargi suna da hanni dumu-duma wajen ta da rikicin.

KU KARANTA : Hukumar lekan asiri ta NIA suna farautar wani Jakadan Najeriya

Babban Sakataren ma’aikatan shari’a na jihar,Kaduna, Mitsa Chris Umaru, ya bayyana haka a ranar Laraba a lokacin da ya zanta da manema labaru a birnin Kaduna.

Bayan haka kotun ta daga zaman ta zuwa ranar 15 ga watan Maris domin ci gaba da shari’ar, sannan ta bada umurnin a ci gaba da daure mutanen kurkuku zuwa wannan rana.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel