Shugaban hukumar 'Yan Sandan Najeriya ya nufi garin Zurmi da ke Jihar Zamfara domin magance matsalar tsaro

Shugaban hukumar 'Yan Sandan Najeriya ya nufi garin Zurmi da ke Jihar Zamfara domin magance matsalar tsaro

- A yau ne babban sufeton 'yan sanda zai je garin zurmi

- Matsalar tsaro na ta ta'azzara a kasar nan

Shugaban hukumar 'Yan Sandan Najeriya ya nufi garin Zurmi da ke Jihar Zamfara domin magance matsalar tsaro
Shugaban hukumar 'Yan Sandan Najeriya ya nufi garin Zurmi da ke Jihar Zamfara domin magance matsalar tsaro

A ranar Asabar dinnan ne Babban Sufeton 'Yan Sandan Najeriya, Ibrahim Kpotun Idris, ya nufi garin Zurmi dake Jihar Zamfara domin shawo kan matsalar tsaro a yankin.

DUBA WANNAN: Wasika ga shugaba Buhari kan yaki da Boko Haram

A ranar Alhamis din da ta gabata ne wasu yan bindiga da ba a san ko su wanene ba, suka kai hari kauyen Birane dake cikin karamar hukumar Zurmi, a jihar Zamfara, inda suka kashe sama da mutune arba'in.

Shugaban hukumar 'yan sandan ya bar garin Lagos a yau Asabar dinnan 17 ga watan Febrairu 2018, ya nufi garin Katsina, inda daga nan zai nufi garin Zurmin dake jihar Zamfara.

Duk da yake ana ganin cewa ire-iren wadannan hare haren sun dan ragu a jihar ta Zamfara, lamarin na kokarin sake dawowa, domin a watan Nuwamba da ya gabata, an kai irin wannan hari a karamar hukumar Mulki ta Shinkafi, inda aka kashe mutane kusan ashirin da hudu tare da kona gidaje da dama.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel