Kannywood: Muna shan wahala matuka wajen samun mazajen aure – Rashida Abdullahi

Kannywood: Muna shan wahala matuka wajen samun mazajen aure – Rashida Abdullahi

Fitacciyar tsohuwar jarumar nan ta fina-finan Hausa a masana'antar Kannywood kuma 'yar siyasa mai suna Rashida Abdullahi ta jadadda cewa suna fuskantar kalubale wajen samun mazajen aure.

Majiyarmu ta kawo inda Jarumar ta kara da cewa: “Samun Mazan Ne Da Wahala, Amma Ko Yanzu Na Samu Miji Da Gudu Za Tayi Aure”.

Kannywood: Muna shan wahala matuka wajen samun mazajen aure – Rashida Abdullahi
Kannywood: Muna shan wahala matuka wajen samun mazajen aure – Rashida Abdullahi

Idan zaku tuna Legit.ng ta kawo a baya cewa jarumar dai ta janye kafar ta daga fitowa a matsayin jaruma a cikin fina-finan Hausa na Kannywood sannan kuma ta tsunduma cikin harkokin siyasa.

KU KARANTA KUMA: An rantsar da sababbin shugabannin kananan hukumomi a Kano

A yanzu haka ma har ta samu mukamin mai bayar da shawara ga Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel