Kungiyar kwallon Barcelona ta kasar Sifen ta kai wa Neymar hari

Kungiyar kwallon Barcelona ta kasar Sifen ta kai wa Neymar hari

- Kungiyar kwallon Barcelona ta kasar Sifen ta kai wa Neymar hari

- Shugaban kungiyar ta Barcelona ne dai Jordi Mestre ya bayyana hakan a yayin wata fira da yayi

- Sun kai masa harin ne bisa yadda ya nemi ya rena masu wayau a karshen kakar wasannin da ta gabata

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona dake a kasar Sifen ta dirar wa shahararren tsohon dan wasan gaban nan na ta kuma dan kasar Brazil wata Neymar Jnr hari bisa yadda ya nemi ya rena masu wayau a karshen kakar wasannin da ta gabata kafin komawar sa kungiyar kwallon kafa ta PSG dake a kasar Faransa.

Kungiyar kwallon Barcelona ta kasar Sifen ta kai wa Neymar hari
Kungiyar kwallon Barcelona ta kasar Sifen ta kai wa Neymar hari

KU KARANTA: Hisba ta kama mabarata a Kano

Shugaban kungiyar ta Barcelona ne dai Jordi Mestre ya bayyana hakan a yayin wata fira da yayi da manema labarai inda ya bayyana cewa inda Neymar din bai nemi ya rena masu wayau ba, da wata kila tsadar sa bata kai hakan ba.

A wani labarin kuma, Labarin da muke samu daga majiyoyin mu ya tabbatar mana da cewa wani dalibi dan ajin karshen a jami'ar gwamnatin tarayya ta fasahar kere-kere dake a garin Akure, jihar Ondo mai suna Tunji Agboola ya fadi ya mutu yana kwallo.

Mun samu dai cewa dalibin ya mutu ne a ranar Asabar din da ta gabata kuma dukkan binciken likitoci ya tabbatar da cewa lafiyar lau kafin ya fara kwallon kuma har yanzu ba'a gano musabbabin mutuwar ta sa ba.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel