Jihohi guda 16 sun amince a tsugunar da Makiyaya da dabbobinsu a cikinsu, ga jerin su nan

Jihohi guda 16 sun amince a tsugunar da Makiyaya da dabbobinsu a cikinsu, ga jerin su nan

Kimanin jihohin guda 16 ne suka yi amanna da tsarin da gwamnatin tarayya ta fitar na samar da wani yanki na daban don amfanin Fulani makiyaya tare da dabbobinsu don hana rikici tsakanin makiyaya da manoma.

Legit.ng ta ruwaito a sakamakon rikita rikitan dake faruwa a tsakanin makiyaya da manoma, wanda yayi sanadiyyar mutuwar jama’a da dama, hakan ne yasa aka kirkiri wannan tsari, daga cikin jihohin da suka amince akwai:

1. Adamawa

2. Kano

3. Kaduna

4. Katsina

KU KARANTA: Najeriya ta samu kudi: NNPC ta samu raran kuɗin mai da ya kai naira biliyan 836 a wata guda

5. Zamfara

6. Kebbi

7. Nasarawa

8. Plateau

Jihohi guda 16 sun amince a tsugunar da Makiyaya da dabbobinsu a cikinsu, ga jerin su nan
Makiyaya

Sauran jihohin da suka yi amanna da tsarin tsugunar da yan Fulani makiyayan da dabbobinsu sune:

9. Bauchi, 10. Gombe, 11. Borno, 12. Jigawa, 13. Yobe, 14. Niger, 15. Kogi da kuma jihar Kwara

Zuwa yanzu an samu jihohin da suka hada da Benuwe, Ekiti, Filato, Fatakwal, Imo da Taraba , wadanda suka nuna adawa karara da wannan tsarin.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel