Kotu ta yanke wa barawon rago hukuncin shekaru biyu a gidan kaso

Kotu ta yanke wa barawon rago hukuncin shekaru biyu a gidan kaso

- Wata kotun Majisatre mai zama a garin Ota ta yanke hukuncin zaman shekaru biyu a gaidan yari kan wani mutum da ya saci rago

- Bayan ya amsa laifin sa, ya ce yunwa ce ta tunzura shi ya aikata satar

- An kiyasta kudin ragon da ya sata a ranar 13 ga watan Janairun 2018 kan N75,000

Kotun Majistare da ke garin Ota a jihar Ogun ta yanke hukuncin zaman gidan kaso har na shekaru biyu ga wani magidanci mai shekaru 37 mai suna Ramon Bello bisa samun sa da laifin satar ragon da kudin sa ya kai N75,000.

Babban Alkali Mr S.O. Banwo ne ya yanke hukuncin bayan Bello ya amsa laifin da ake tuhumar sa da ita, alkalin bai bayar da zabi na biyan tara ba.

Kotu ta yanke wa barawon rago hukuncin shekaru biyu a gidan kaso
Kotu ta yanke wa barawon rago hukuncin shekaru biyu a gidan kaso

Bello da ke zaune a gida mai lamba 14 layin Bamidele a garin Ota ya shaida wa kotu cewa yunwa ce ta ingiza shi aikata satar.

KU KARANTA: Buhari ya ci zaben 2019 ya gama - Sakataren gwamnatin tarayya

Mai shigar da kara, Sajent Chudu Gbesi ya fadawa kotu cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin ne a ranar 13 ga watan Janairu misalin karfe 5:30 na yamma a tashan shiga mota na kwalejin Bible na garin Ota.

Gbesi ya kara da cewa ragon da Bello ya sace mallakin Kehinde Yekinni ne kuma an kiyasta kudin ragon a N75,000.

Mai shigar da karar ya ce laifin ya saba wa sashi na 390(9) na dokar masu laifi na jihar Ogun na shekarar 2006.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel