LABARI DA DUMI-DUMI: El-Zakzaky a karon farko ya gana da manema labarai

LABARI DA DUMI-DUMI: El-Zakzaky a karon farko ya gana da manema labarai

- Sheikh El-Zakzaky a karon farko ya gana da manema labarai

- Kafar watsa labarai ta PR Nigeria ta aiko da hotunan shugabn IMN a yayin da yake ganawa da manema labarai

- El-Zakzaky ya bayyana cewa yana nan a raye kuma yana cikin koshin lafiya

Shugaban kungiyar 'yan Uwa Muslumi wato Islamic Movement in Nigeria (IMN) wanda da aka fi sani da Shi'a, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, a karo na farko ya gana da manema labarai tun bayan da jami’an tsaro suka kama shi.

Idan dai baku manta rundunar sojin Najeriya ce ta kama Sheikh El-Zakzaky a watan Disambar shekarar 2015 a garin Zaria da ke jihar Kaduna, bayan wani rikici tsakani ‘ya’yan kungiyar da sojoji wanda ta yi sanadiyar lalata gidansa.

Kamar yadda Legit.ng ke da labari, a wata sanarwa da kafar watsa labarai ta PR Nigeria ta fitar, ta ce shugaban kungiyar ya yi magana da 'yan jarida.

LABARI DA DUMI-DUMI: El-Zakzaky a karon farko ya gana da manema labarai
Shugaban kungiyar 'yan Shi'a, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky

A sanarwar, an turo da hotunansa a yayin da yake ganawa da manema labarai.

KU KARANTA: Shugaban shi'a El-Zakzaky bai mutu ba, yana nan a raye - IMN

A wata rahoto kuma gidan talbijin na Channels ita ma ta ce Malamin ya bayyana cewa yana nan a raye kuma yana cikin koshin lafiya.

Ku biyo mu dan samun karin bayani ...

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa Wannan: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel