Za mu gina hanyar jirgin kasa daga Kano zuwa Maradi – Shugaba Buhari

Za mu gina hanyar jirgin kasa daga Kano zuwa Maradi – Shugaba Buhari

- Gwamnatin Buhari za ta gina hanyar jirgi zuwa cikin Kasar Nijar

- Yanzu haka Shugaban Kasar yace ana tattaunawa ne kan maganar

- Hanyar jirgin za ta ratsa tun daga Kano ya bi ta Daura har Maradi

A safiyar mu ka samu labari mai dadi a jawabin murnar shiga sabuwar shekarar da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya gabatar inda yace za a fitar da hanya daga Najeriya zuwa Nijar. Dama dai ana cigaba da wasu aikin jirgin kasa a Najeriya.

Za mu gina hanyar jirgin kasa daga Kano zuwa Maradi – Shugaba Buhari
Shugaba Buhari zai gina hanyar jirgi zuwa Maradi

Shugaban Kasar yace Gwamnatin sa za tana kokarin ganin ta shimfida hanyar jirgin Kasa ne daga Najeriya zuwa Kasar Jahmuriyyar Nijar. Za a tado aikin ne tun daga Jihar Kano zuwa Jihar Maradi da ke Nijar. Yanzu haka dai ana kan maganar ne.

KU KARANTA: Buhari ya koka da halin da rashin mai ya jefa wasu a Kasar

Hanyar jirgin da za ayi, zai faro daga Kano ne inda zai shiga Kazaure daga nan yayi Kasar Daura zuwa Garin Jibiya da ke kan iyaka a Jihar Katsina. Daga nan layin jirgin kasan zai tike a Jihar Maradi da ke cikin Kasae Jamhuriyyar Nijar.

Dama dai Shugaban Kasa Buhari yayi wannan jawabi ko kwanakin baya da ya kai ziyara Jihar Kano inda yace za a fara gyara hanyoyin cikin gida tukunna kafin a kai ga maganr jirgi zuwa Nijar. A bana dai za a ga tulin ayyuka a Kasar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel