Wayar wutar lantarki ya kashe mutum daya, da kona gidaje shida a Calabar

Wayar wutar lantarki ya kashe mutum daya, da kona gidaje shida a Calabar

- A ranar jajibarin sabuwar shekara 2018, wayar wutar lanatarki ya kashe mutum daya a Calabar

- Sau uku wutan lantarki yana kashe mutane a cikin shekara daya a garin Calabar

Sau uku kenan wayar wutar lantarki yana kashe mutane a cikin shekara daya a Calabar, jihar Cross River.

A ranar Lahadi ne wayar wutar lanatarki yayi sanadiyar mutuwar mutum daya da lalata gidaje shida a Calabar.

Al’amarin ya faru ne, a ranar Lahadi da misalin karfe 7.30 na yamma wanda ya raunana mutane biyu a gida mai lamba 17 Umo Orok Lane Calabar.

Wayar wutar lantarki yayi sanadin mutuwar mutum daya, da lalata gidaje shida a Calabar
Wayar wutar lantarki yayi sanadin mutuwar mutum daya, da lalata gidaje shida a Calabar

A ranar, 20 ga watan Maris, 2017, mutane takwas suka rasa rayukan su ta sanadiyar fadowar wayar wutar lantarki a samar rufin gidan kallon kwallo a lokacin da mutane ke kallo wasan kwallo a jihar Edo.

KU KARANTA : Masar ta yanke wa tsohon shugaban kasa Morsi tare da mutane 19 shekaru uku a gidan kaso bisa laifin zagin hukumar shari'ar kasar

Bayan haka a watan Oktoba na shekara 2017 wayar wutar lantarki ya kara kashe mutane biyu a unguwar Adak Uko dake Calabar da kona gida daya.

Rahotanni sun nuna cewa, karfin wutar lantarki ya janyo mumunar hatsarin da ya faru a ranar Lahadi, wanda yayi sanadiyar konewar gidaje shida da kashe wani matashi dan kasuwa mai suna Joseph.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa Wannan: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel