Gwamnatin Iran tayi barazanar babban taku muddin zanga-zanga bata tsaya ba

Gwamnatin Iran tayi barazanar babban taku muddin zanga-zanga bata tsaya ba

- Ana zanga-zangar kin jinin gwamnati a biranen Iran

- Mabiya gwamnati suma sun fito nuna soyayyarsu ga shugabanninsu

- Gwamnati tace masu adawa su koma gida ko su fuskanci hukuma

Gwamnatin Iran tayi barazanar babban taku muddin zanga-zanga bata tsaya ba
Gwamnatin Iran tayi barazanar babban taku muddin zanga-zanga bata tsaya ba

Kasar Iran ta shiga kwana na ukku ana buga zanga-zanga a manyan biranen kasar ta, wanda aka faro ranar juma'a, kuma har an fara samun asarar rayuka.

A jiya kuma masu biyayya ga gwamnati suma sun fito a babban birnin domin nuna soyayya ga shugaba Rouhani da ma Mista Khamenei, babban limamin kasar.

Sai dai gwamnati a yau tayi kira da masu adawa da zanga-zanga da su koma gida ko su fuskanci fushin hukuma, kamar yadda BBC ta ruwaito.

DUBA WANNAN: Wani mai ikirarin annabta ya ce ya gano gobe

Tun a 2009 da aka yi irin wannan muzahara, wadda da yawa suka mutu, ba'a kara samun irin wannan tashin-tashina da ta kai wannan girma ba, kuma hukumomi basu so kasar ta shiga rikici kamar yadda ta faru a sauran kasashen yankin.

Masu zanga-zangar dai na kira da a kawo karshen matsin tattalin arziki, da tsauraran matakai dagwamnati ke dauka kan 'yancin 'yan kasa da sunan addini, musamman mika kudaden kasar ga mayaka a wasu kasashen, maimakon habaka arzikin cikin gida.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel