Jirgin mata zalla na farko zai sauka Najeriya daga kasar Habasha

Jirgin mata zalla na farko zai sauka Najeriya daga kasar Habasha

Ana sa ran saukar jirgi mai dauke da mata zalla a Najeriya a ranar Asabar. Jirgin ya kasance na kasar Habasha wato Ethiopian Airlines.

A cewar kungiyar kamfanin jirgin sama, mata zasu cike dukka nmatakai a jirgin; abinda ya kama daga matuka da ma’aikatan cikin jirgin, har da masu aikin kula da gangarar jirgin da masu balaguro a kasar.

Wannan zai kasance karo na farko da ET zata gudanar da aikin jirgi na mata zalla a Afirka.

A wani jawabi da aka kaddamar a Legas, kamfanin jirgin saman tace jirgin zai tashi daga Addis Ababa, babbar cibiyar ayyukan jirage, a ranar 16 zuwa tashar jirgin Murtala Muhammed International Airport (MMIA), dake jihar Legas.

Jirgin mata zalla na farko zai sauka Najeriya daga kasar Habasha
Jirgin mata zalla na farko zai sauka Najeriya daga kasar Habasha

Matukiyar jirgin, Captain Amsale Gualu, ta yi tukin jirgi zuwa sauran yankuna a baya.

KU KARANTA KUMA: Mataimakin shugaban kasa ya jagoranci zaman majalisa (hotuna)

Jirgin mata zallan na da Tigist Kibret a matsayin matukiyar ta na farko, wacce zata tuka jirgin mai suna Boeing 777.

A kasar inda mata kalilan suka shiga sana’an tukin jirgin sama wacce mafi yawanci maza ne, Captain Gualu, a 2010 ta kasance mace ta farko a kasar Habasha da tayi tuki daga Addis Ababa zuwa Gondar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel