Adam Zango ya yaba da bajintar Fati Washa wajen rera wakar Gwaska

Adam Zango ya yaba da bajintar Fati Washa wajen rera wakar Gwaska

- Fati Washa ta taya Adam Zango tallata fim dinsa dake shirin shiga kasuwa

- Tayi hakan ne ta hanyar rera wakar fim din a shafinta na Instagram

- Zango yayi matukar yaba wa bajintar ta

Fittaciyyar jarumar nan dake wasa a fina-finan Hausa, Faati Washa ta shiga layin dubban masoyan jarumin jarumai Adam Zango wajen tallata sabon fim dinsa da ya kusa fitowa kasuwa wato ‘Gwaska’.

Jarumar ta rera wakar cikin kwarewa ka ce it ace ta rubuta shi. Fati ta nuna bajintar nata ne a wani bidiyo da ta yi sannan ta wallafa a shafinta na Instagram.

Adam Zango ya yaba da bajintar Fati Washa wajen rera wakar Gwaska
Adam Zango ya yaba da bajintar Fati Washa wajen rera wakar Gwaska

Ta faro wakar daga farko har karshe inda har shi kansa Zango da ya shirya fim din sai da ya yaba.

KU KARANTA KUMA: Gwamnatin tarayya ta sanar da gurbin aiki a ma’aikatun tarayya

Gwaska dai fim ne da ba ataba irin sa ba a farfajiyar Kannywood, saboda tsara shi da akayi da kuma irin abubuwan da akayi a fim din na gani na fada.

Zango ya sanar cewa zai gana da masoyan sa na Kano da ya hada da mata 15 maza 15 da suka fafata a gasar wakar fim din da ya sa a yi domin nuna wa kowa cewa alkawarin da ya dauka zai cika shi.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel