Ta tabbata: Akwai bata-gari a cikin ‘Yan fim da dama – Adam Zango

Ta tabbata: Akwai bata-gari a cikin ‘Yan fim da dama – Adam Zango

- Adam Zango yace akwai mutanen banza a ‘yan fim

- Dan wasan yace ana buga fasikanci na kin karawa

- Tauraron yace akwai fa gyara a harkar kannywood

Mun samu labari cewa babban Dan wasan nan Adam A Zango ya kalubalanci ‘Yan fim din Hausa inda yace akwai gyara.

Ta tabbata: Akwai bata-gari a cikin ‘Yan fim da dama – Adam Zango
Tauraron Dan wasa Adam Zango

Gwarzon ya tabbatar da cewa dai akwai bata-gari a cikin ‘Yan fim da dama kamar yadda ake samun na banza a ko ina a Duniya. Dan wasan ya tabbatar da cewa wasu ne su ka jawo wasu har ta kai ake kiran su jahilai da sauran su a fagen fim.

KU KARANTA: Saudi za ta bude wani tashan jirgin sama

Adam Zango ya kuma bayyana cewa masifar da ke cikin Kannywood ta wuce duk yadda ake tunani inda yace ana buga zalunci da fasikanci iri-iri. Yace sai ka ga yara daga fara fim sun kuma bude na su kamfanin har sun zama manya.

Zango ya bayyana wannan ne a shafin sa na Facebook inda yace idan fa abin da ya fada karya ne sai a tona masa asiri amma shi ba zai kama sunan kowa ba.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel