Babban dalilin da ke sa karuwanci na karuwa a Najeriya - Malamin addini

Babban dalilin da ke sa karuwanci na karuwa a Najeriya - Malamin addini

Wani malamin addinin kirista mai suna Fasto Samuel Adegboye ya yi tir tare da tofin Allah-tsine musamman ma ga yadda yace karuwanci a tsakanin kananan yara mata a ta kara yin yawa a kasar nan ta Najeriya sannan kuma yayi kira ga gwamnatin tarayya da ta haramfa kazamar sana'ar.

Fasto Adegboye wanda kuma shine shugaban rukunin coci-coci na General Overseer of Testimony Chapel na garin Ilori ya kuma ja hankalin gwamnatocin kasar a kowane mataki da su tabbatar da sun samar wa matasa ayyukan yin wanda rashin sa ne ke jefa su cikin sana'ar ta karuwancin.

Babban dalilin da ke sa karuwanci na karuwa a Najeriya - Malamin addini
Babban dalilin da ke sa karuwanci na karuwa a Najeriya - Malamin addini

KU KARANTA: An fitar da wata 'yar majalisa waje saboda shigar banza

Legit.ng ta samu dai cewa shehin malamin ta Kiristanci yayi wannan jawabin ne a garin Ilori inda kuma ya bayyana cewa duk macen da ta maida karuwanci a matsayin sana'a to kam tabbas tabewar duniya ta gama sauka a kanta.

A baya ma dai mun kawo maku wani labarin yadda jama'a mazauna garin Abuja babban birnin tarayya ke kokawa game da yawaita karuwai da kuma 'yan daudu a garin yayin da kuma suka bukaci Gwamnati da ta shigo cikin lamarin domin yiwa abun tufka.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel