Harshen damo: Shararen mai garkuwa da mutane Evans ya musanta tuhumar da ake masa

Harshen damo: Shararen mai garkuwa da mutane Evans ya musanta tuhumar da ake masa

- Ya musanta tuhumar ne alhali a baya ya amsa tuhumar

- Lauya mai kare shi ya nemi a daga shari'ar zuwa wani lokaci

- Alkali mai sharia O.H. Oshodi na kotun ya daga shari'ar zuwa 3 ga watan Nuwamba

A yau ne Alhamis, 19 ga watan Nuwamba, Gawurtaccen mai yin garkuwa da mutane da aka fi sani da Evans ya musanta tuhumar da ake masa a yayin da shari'ar ta sa ta cigaba a babban kotun Ikeja na Jihar Legas.

Shi da sauran mutum 5 da ake zargi, wanda 1 daga cikin su mace ce, duk sun musanta tuhumar a gaban Alkali mai shari'a O.H. Oshodi bayan an yi kwaskwarima ga tuhumar da ake masu, alhali a wancan zaman shari'ar da a ka yi sun amsa tuhumar.

Harshen damo: Evans ya musanta tuhumar da ake masa
Harshen damo: Evans ya musanta tuhumar da ake masa

Daga nan ne Lauya mai kare wadanda ake tuhumar ya roki alkalin da ya daga shari'ar. Alkalin kuwa ya amsa rokon na sa ya daga shari'ar zuwa 3 ga watan Nuwamba.

DUBA WANNAN: Yankin Quebec na Kasar Canada ta hana sanya nikabi

Legit.ng ta na harabar kotun a inda ta shaida yadda aka tsananta matakan tsaro saboda wannan shari'ar. Legit.ng kuma ta kawo maku yadda aka gurfanar da shi Evans din da sauran wadanda ake zargi a wannan kotun.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel