Takaicin maza ne ke sanya matan Katsina shiga shaye shaye – Saulawa

Takaicin maza ne ke sanya matan Katsina shiga shaye shaye – Saulawa

- Wata matashiya ta bayyana daliln da yasa mata ke shiga harkar shaye-shaye a jihar Katsina

- A cewarta takaicin maza ke haddasa hakan

- Saulawa tace idan ba’a shawo kan wannan matsala cikin gaggawa ba, za’a samu karin tabarbarewa tarbiya

Wata matashiya a jihar Katsina da aka ambata da suna Khadija Saulawa ta bayyana yadda takaicin maza a ke sanya matan jihar shaye-shaye.

Saulawa, ma'assashiyar wata kungiya mai zaman kanta ‘Queen Dijah Women and Children Awareness Initiative’ tace kudirin ta shine ta wayar da kawunan mata akan illolin dake tattare da wannan harka.

A wata zantawa da tayi da jaridar Vanguard, Saulawa tace idan ba’a shawo kan wannan matsala cikin gaggawa ba, za’a samu karin tabarbarewa tarbiya a nan gaba.

Takaicin maza ne ke sanya matan Katsina shiga shaye shaye – Saulawa
Takaicin maza ne ke sanya matan Katsina shiga shaye shaye – Saulawa

Saboda a cewar ta “Idan kullum uwa na cikin maye wa zai kula da yara?”

KU KARANTA KUMA: Mambobin kungiyar IPOB sunyi zanga-zanga a ofishin jakadancin Turai dake Jamus

Ta ce yawanci mata na shiga harkar shaye-shaye ne da zaran an fada masu cewa zai kawar masu da bakin cikin da mazajen su suka sanya su a ciki. Ta ce da sun dandana suka ji dadi, shikenan ba za su iya dainawa ba.

Saulawa ta kuma ce kungiyar ta ta za ta mayar da hankali a bangaren fyaden kananan yara, wanda ta ce shi ma ya zama ruwan dare a Katsina da samar da tsaftataccen ruwan sha.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel