Mahaukaciya da ta haihu ta samu tallafi daga gwamnati (hotuna)

Mahaukaciya da ta haihu ta samu tallafi daga gwamnati (hotuna)

- Wata mahaukaciya da ta haifi ‘ya mace ta samu tallafi daga karamar hukumar

- An dauki ‘yar da matar ta haifa zuwa gidan marayu

- An mayar da matar asibitin kwakwalwa

Wata karamar hukuma a jihar Ondo ta bayar da tallafi ga wata mahaukaciya da ta haihu a yankin Yaba dake jihar.

Legit.ng ta tattaro cewa hukumomin karamar hukumar Idanre sun kai doki ga wata mata bayan ta haifi ‘ya mace.

A cewar wani mai amfani da shafin Facebook, Jimoh Ibrahim, karkashin shugabancin mai girma Adebiyi Ayannuola, an dauki jaririyar zuwa gidan marayu.

Mahaukaciya da ta haihu ta samu tallafi daga gwamnati (hotuna)
Mahaukaciya da ta haihu ta samu tallafi daga gwamnati. Hoto: Jimoh Ibrahim

KU KARANTA KUMA: Ina da wani buri! Kalli bidiyon Maitama Sule yana magana kafin mutuwar shi

Ibrahim ya kara da cewa an kuma dauki mahaifiyar yarinyar zuwa asibitin kwakwalwa don bata kulawa na mussaman.

Mahaukaciya da ta haihu ta samu tallafi daga gwamnati (hotuna)
An kai yarinyar gidan marayu yayinda aka dauki mahaifiyar yarinyar zuwa asibitin kwakwalwa don bata kulawa na mussaman. Hoto: Jimoh Ibrahim

Matar shugaban karamar hukumar Idanre, Doyin Ayannuola da mai kula da sashin lafiya, Aderonke Akindolire, ne suka jagoranci kula da mayar da jaririyar da uwarta inda ya kamata.

Mahaukaciya da ta haihu ta samu tallafi daga gwamnati (hotuna)
Matar shugaban karamar hukumar Idanre, Doyin Ayannuola da mai kula da sashin lafiya, Aderonke Akindolire, ne suka jagoranci kula da mayar da jaririyar da uwarta inda ya kamata. Hoto: Jimoh Ibrahim

Kalli rubutun a kasa:

Abu ya yi kyau!

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel