Abubuwan tarihi 11 dangane da marigayi Dan Masanin Kano-KARANTA

Abubuwan tarihi 11 dangane da marigayi Dan Masanin Kano-KARANTA

- Shahararren dattijon yankin Arewa, Maitama Sule ya rasu a kasar Masar

- Kafin rasuwarsa, Maitama Sule na daya daga cikin yan Arewa masu mutunci a idon Jama’a

A yau Litinin 3 ga watan Yuli ne Allah yayi ma Dan Masanin Kano, Alhaji Maitama Sule rasuwa a kasar Masar inda ya kwashe lokaci yana jinya.

Legit.ng ta kawo muku wasu daga cikin muhimman abubuwan tarihi dangane da marigayi Maitama Sule:

KU KARANTA: Abin da ya sa ba za a taba mantawa da Dan Masanin Kano ba

1- A birnin Kano aka haife Maitama Sule, kuma yana da marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero ya nada shi sarautar Dan Masanin Kano.

Abubuwan tarihi 11 dangane da marigayi Dan Masanin Kano-KARANTA
Dan Masanin Kano

2- An haifi Maitama Sule a shekarar 1929, kuma ya rasu yana da shekaru 87.

3- Yana da shekaru 24 ne ya zama dan majalisar wakilai, sa’annan yana dan shekaru 29 ya zama minista.

Abubuwan tarihi 11 dangane da marigayi Dan Masanin Kano-KARANTA
Dan Masanin Kano

4- Shakikan aminansa sune marigayi Sarkin Kano, Ado Bayero, marigayi galadiman Kano, Tijjani Hashim da kuma Alhaji Aminu Dantata.

5- Shine mutumin da yafi dadewa a matsayin ministan mai ba tare da mallakar rijiyan mai ko daya ba.

Abubuwan tarihi 11 dangane da marigayi Dan Masanin Kano-KARANTA
Dan Masanin Kano

6- Maitama yak ware a yarukan Hausa, Ingilishi, Larabci da Fillanci

7- Mutanen dayake koyi dasu sun hada da Tafawa Balewa, Obafemi Awolowo, Nnamdi Azikwe da kuma Malam Aminu Kano.

8- Ya zama kwamishinan karban koke-koke da korafi na gwmanantin tarayya a shekarar 1976, zamanin mulkin Obasanjo na farko.

Abubuwan tarihi 11 dangane da marigayi Dan Masanin Kano-KARANTA
Dan Masanin Kano

9- A shekarar 1979 yayi takarar shugabancin kasar nan a karkashin jam’iyyar NPN, amma ya sha kashi a zaben cikin gida a hannun Alhaji Shehu Sahagari.

10- A wannan shekarar ne aka nada shi mukamin wakilin Najeriya na dindindin a majalisar dinkin Duniya.

11- A shekarar 1983 ne ya dawo gida Najeriya, inda aka nada shi mukamin ministan daidaita sahun yan Najeriya.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Shin zaka iaya agaza ma Buhari ya samu lafiya?

Asali: Legit.ng

Online view pixel