Garabasa: Ina mai neman gafara da biyan bukata cikin watan Ramadan

Garabasa: Ina mai neman gafara da biyan bukata cikin watan Ramadan

– An shiga kwamakin goman karshe a cikin wannan wata

– A yanzu ne za a dace da daren Lailatul Qadr mai albarka

– Ana kuma son a shiga ibadar I’itikafi a halin yanzu

Kun san cewa akwai lada ga wanda ya samu yin I’itikafi a cikin wannan wata. Manzon Allah SWT ya kan yi wannan ibada a masallacin sa. Ana so Musulmai su dage domin su dace da daren Lailatul Qadr.

Garabasa: Ina mai neman gafara da biyan bukata cikin watan Ramadan
Shugabannin Najeriya cikin sallah

Akwai Hadisi daga Manzon Allah SAW da ke cewa duk wanda yayi I’itikafi a kwanaki goma na karshen Ramadan ba zai shiga wutar Jahannama ba. Wannan Hadisi dai Imam Tabarani ya kawo shi.

KU KARANTA: Falalar da ke cikin daren Lailatul Qadr

Garabasa: Ina mai neman gafara da biyan bukata cikin watan Ramadan
Ana so Musulmai su dage domin su dace da Lailatul Qadr

Haka kuma ana sa ran ganin daren nan mai albarka a cikin ‘yan kwanakin nan, Manzon Allah ya tabbatar da cewa lallai za a samu wannan Lailatul Qadr a cikin dararen da mu ka shiga kuma musamman a kwanaki na mara watau daren 21, 23, 25, 27 da kuma daren azumi na 29.

A yau dai da mu ke magana muna daren 21 ne don haka ana sai daren ya shigo a wannan rana. A wannan dare ne dai Allah zai yafewa bayin sa da su ka nemi gafara.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Har yanzu Najeriya na da wani matsayi a Afrika ?

Asali: Legit.ng

Online view pixel