Yadda Sarki Sanusi I ya bar gadon sarauta a 1963

Yadda Sarki Sanusi I ya bar gadon sarauta a 1963

– Sarki Muhammadu Sanusi II ya tabo tsuliyar dodo kwanakin baya

– Wasu na ganin ana yi sauke sa daga kujerar a nada wani sabon Sarkin

– Haka dai aka yi wa Kakan sa a shekarar 1963

Idan ba ayi wasa ba za a iya sauke Sarkin Kano kamar yadda aka sauke Kakan sa.

Kujerar Sarki Sanusi II tana rawa bayan da aka shiga binciken fadar sa.

Haka aka yi da Kakan sa Sanusi I bayan ya samu matsala da masu mulki a lokacin sa.

Yadda Sarki Sanusi I ya bar gadon sarauta a 1963
Barewa za tayi gudu 'Dan ta yayi rarrafe: Sarki Sanusi II ya tsokano manya

An ce a wancan lokacin rikicin ya fara ne cikin gida bayan da daya daga cikin ‘Ya ‘yan Sarki Sanusi I ya saki matar sa wanda Diya ce wurin Sarkin Gwandu kuma ‘Yaruwar Sardauna. Sarkin ya kuma nemi ya ja da Sardaunan akan wasu dokoki da aka kafa.

KU KARANTA: Sarki Sanusi ya gargadi Shugabanni

Yadda Sarki Sanusi I ya bar gadon sarauta a 1963
Ko shin Sarki Sanusi II zai sha ko shi ma za ayi masa irin na Kakan sa?

A lokacin da aka yi dokar da ta karbe ikon filaye daga hannun Sarakuna dai Sarki Sanusi I bai ji dadin hakan ba. Wanda wannan ya kara jagwalgwala alakar su har ta kai aka tsige sa daga Sarautar inda ya koma Kasar Azare da zama.

Mun samu kishin-kishin kwakanaki cewa wasu daga cikin Gwamnonin Arewa sun yi wani taro game da Sarkin Kano a kasar China inda su ka nemi a tsige sa saboda irin cin fuskar da yake masu sai dai da alamu an sasanta Sarkin da Gwamnan Jihar Kano.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Muna cikin matsala a Najeriya

Asali: Legit.ng

Online view pixel