Jay Jay Okocha na Najeriya ne gwani na-Inji Ronaldinho

Jay Jay Okocha na Najeriya ne gwani na-Inji Ronaldinho

– Tsohon Tauraron Duniya Ronaldinho yace shagon sa shi ne Okocha na Najeriya

– Ronaldinho yace ba a taba lamba 10 da ya burge sa irin Okocha ba

– ‘Yan wasan sun taka leda tare a Kungiyar PSG.

Dan wasan kasar Brazil Ronaldinho yace Okocha ne shagon sa a kwallo.

Tsohon Dan wasan na Barcelona in dai lamba 10 ake magana sai Okocha

Ronaldinho ya zama gwarzon Duniya har sau 2 a jere.

Jay Jay Okocha na Najeriya ne gwani na-Inji Ronaldinho
Austin Jay Jay Okocha tare da Ronaldinho

Tsohon Dan wasan Duniya na kasar Brazil Ronaldinho yace tun da yake kwallo bai taba ganin ‘Dan wasan da ya burge sa ba irin Austin Jay-Jay Okocha na Najeriya. Ronaldinho sun hadu ne da Okocha kwanan nan a kasar Bahrain.

KU KARANTA: FIFA za ta binciki ciniki Pogba

Jay Jay Okocha na Najeriya ne gwani na-Inji Ronaldinho
Jay Jay Okocha na burge ni-Ronaldinho

Manyan ‘Yan wasan sun buga wasa tare a Kungiyar PSG ta kasar Faransa kuma ba mamaki Ronaldinho ya koyi darasi wurin tsohon Kyaftin din na Najeriya. Ronaldinho ya saka wani hoto da suka dauka tare a shafin san a Instagram.

Duk da Real Madrid ta sha kashi a hannun makwabtan ta Atletico Madrid ta isa wasan karshe. Watakila Real Madrid din tayi abin da ba a taba yi ba bana idan ta kara Juventus an yi mai-man abin da ya faru a shekarar 98.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Dubi abin da wata Budurwa ke yi

Asali: Legit.ng

Online view pixel