Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya

Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya

Tsohuwar ministar muhallin Buhari daga jihar Adamawa kuma sabuwar mataimakiyar Sakatare Janar na majalisar dinkin duniya tayi wani dogon bayani mai rasta jini a jawabin ta na farko a majalisar.

Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya
Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya

An dai ruwaito cewar Amina Muhammad ta yi bayain ne mai cike da hikima da basira a cikin satin da ya gabata yayin da take shan rantsuwar kama aiki a majalisar.

A cikin jawabin nata, Amina Muhammad wadda ta fito daga arewacin Najeriya tace dole ne majalisar ta dinkin duniya ta shirya tsaf kuma tayi adalci idan dai har tana so a rika daratta ta.

KU KARANTA: Sabon sako daga Osinbajo

Hakama ta jinjinawa Sakataren na majalisar saboda yadda da yayi da ita yayin da kuma ta sha alwashin ba mara da kunya a aikin nata.

Mai karatu dai zai tuna cewa, Sakatare-Janar na majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres, ya nada Ministar muhalli ta Najeriya Amina Mohammed a matsayin mataimakiyarsa.

Mista Guterres ya kuma nada wasu mata biyu a wasu manyan mukamai a majalisar.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel