Sabon shugaban Gambia ya dawo gida

Sabon shugaban Gambia ya dawo gida

– Sabon shugaban kasar Gambia Adama Barrow ya dawo gida

– Adama Barrow ya shigo Kasar sa bayan Yahaya Jammeh ya fita

– Barrow ya baro Kasar Sanagal inda ya labe

Sabon shugaban Gambia ya dawo gida
Sabon shugaban Gambia ya dawo gida

Sabon shugaban Kasar Gambia da aka zaba a karshen bara, Adama Barrow ya taba Kasar Gambia. A jiya ne Barrow ya shigo Garin Banjul na Kasar ta Gambia, bayan da shi kuma Yahaya Jammeh ya bar Kasar.

Kamar yadda BBC ta fada, Jama’a sun yi dafifi a filin jirgi inda suke jiran sabon shugaban na su Adama Barrow ya iso. Barrow dai ya dade a labe a Kasar Senegal tun bayan da aka zabe sa, kafin a rantsar da shi.

KU KARANTA: Aikin Shugaba Buhari na kyau?

An dai ga Sojojin Najeriya suna sintitiri yayin da Barrow ya shigo Kasar. Dakarun ECOWAS dai suka matsawa Jammeh har sai da ya sauka daga mulkin bayan ya fadi zabe, ba dan yana so ba. Jammeh ya fi shekaru 20 yana mulkin Kasar Gambia.

Da alamu dai tsohon Shugaban Kasar Gambia, Yahaya Jammeh zai cigaba da rayuwar jin dadi ne ko a zaman gudun hijirar da zai yi. An dai bar Jammeh ya tafi da ingaramammun motocin har guda 13 zuwa Kasar Equatorial Guinea inda zai yi zaman san a Gudun Hijira.

A biyo mu a shafin mu na Tuwita http://twitter.com/naijcomhausa da kuma Facebook

https://www.facebook.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel