Wacece matar sabon Gwamnan Jihar Ondo?

Wacece matar sabon Gwamnan Jihar Ondo?

- Ko ka san Uwargidar Gwamna mai jiran gado, Misis Akerodolu

- An kammala zaben Jihar Ondo, inda dan takarar APC yayi nasara da kuma Rotimi Akerodolu ne ya lashe zaben

Wacece matar sabon Gwamnan Jihar Ondo?

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Ko shin wacece Misis Akeredolu? Mai dakin sabon gwamnan jihar Ondo, mai jiran gado? Mun kawo maku abubuwa 5 da ba ku sani ba game da Ran ta ya dade, Misis Betty Akeredolu:

Matar Sabon Gwamnan Jihar Ondo, mai jiran gado mutumiyar kasar Inyamurai ce. Nee Anyawu ta fito daga Emeabiam, Owerri a jihar Imo.

Misis Betty Akeredolu tayi fama da cutar cancer na mama a baya. Tuni yanzu ta murmure, har ta bude Kungiya mai kula da irin wannan cuta.

KU KARANTA: Akeredolu ya lashe zaben Jihar Ondo

Matar Gwamnan mai jiran gado a Jihar Ondo tana da digiri har biyu a kan fannin noman dabbobi. Tayi karatun kiwon kifi a Kasar Philippines, tana kuma da gona a Ibadan.

Misis Betty tana shekaru fiye da 60 a duniya, kuma tana da ‘ya ‘biyar, ciki guda na da aure, don haka tana da jika.

Wacece matar sabon Gwamnan Jihar Ondo?

 

 

 

 

 

Kullum tana bayan Mijin ta, ko a wajen yakin neman zaben nan, da ita aka yi tafiyar tun shekaru hudu da suka wuce.

A biyo mu a shafin mu na Tuwita @naijcomhausa    

 

https://youtu.be/wXmmTEAKDxo

Asali: Legit.ng

Online view pixel